in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta ci gaba da neman jirgin sama da ya bace na Malaysia
2014-04-02 20:52:49 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya bugawa takwaransa na kasar Austriliya Tony Abbott a safiyar laraban nan 2 ga wata, inda ya bayyana cewa, ana fuskantar wawuyacin mawuyacin hali wajen gudanar da aikin neman jirgin da ya bace amma duk da haka ba za a yi sanyi a gwiwwa ba ko kadan.

Mr Li ya yi bayanin a lokacin zantawar su cewa Sin ta tura jiragen ruwa fiye da 10, kuma jiragen saman kasar da dama suna yin hadin kai da sauran na kasa da kasa domin nema da gano duk wata shaida na abubuwan da ka iya nuna tarkacen jirgin ne.

Ban da wannan kuma, jiragen ruwan masu zaman kansu na kasar Sin wadanda suka ratsa wannan yanki da jiragen ruwan kamun kifaye 20 suma sun shiga aikin neman jirgin.

A ta bakin kakakin ma'aikatar harkokin waje na kasar Sin Hong Lei lokacin ganawar sa da manema labarai a nan birnin Beijing a safiyar yau ya ce kasar ta bayyana matsayin data dauka a game da kokarin da ake yi na neman jirgin saman da ya bace.

Kuma Kasar Sin zata cigaba da neman wannan jirgin saman da ya bace domin yYa zuwa yanzu kasar ta tura jiragen ruwan yaki 7 domin su cigaba da gudanar da aikin a kan teku.. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China