in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude sabon shafi na neman jirgin fasinjan nan da ya bace
2014-03-30 16:29:43 cri
Mahukuntan kasar Austireliya, sun kafa wata sabuwar cibiyar binciken jirgin fasinjan nan na kasar Maleshiya da ya bace sama da makwanni Biyu da suka gabata.

A cewar Firaministan kasar ta Austreliya Tony Abbott, tsohon jami'in rindunar sojin saman kasar Angus Houston ne zai jagoranci cibiyar ta hadin gwiwa da akaiwa lakabi da JACC mai sansani a Perth.

Ana sa ran dai wannan cibiya, zata dauki nauyin kula, tare da aiwatar da tallafin gwamnatoci, a aikin laluben wannan jirgi da ake ci gaba da yi yanzu haka. Haka zalika, cibiyar zata yi aiki kafada da kafada, da daukacin masu ruwa da tsaki, ciki hadda 'yan uwa da iyalan fasinjojin dake jirgin, da kuma 'yan jaridar kasa da kasa.

Kawo yanzu dai jiragen saman kasashen Austreliya, da Sin, da Japan, da na Malashiya na ci gaba da neman baraguzan jirgin da ake zaton ya fadi a yamma da gabar ruwan birnin Perth na yammacin Australiya. Sauran kasashen dake tallafawa aikin sun hada da New Zealand, da Koriya ta Kudu da kuma kasar Amurka.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China