in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabbin ministocin kasar Masar sun yi rantsuwar kama aiki
2014-03-02 19:32:47 cri
Sabbin ministocin kasar Masar a karkashin jagorancin sabon firaministan kasar Ibrahim Mahlab, sun yi rantsuwar kama aiki a yammacin ran asabar 1 ga watan Maris din nan.

Ibrahim Mahlab wanda ya yi murabus daga mukamin ministan gidaje na gwamnatin wucin gadi a ran 24 ga wata Fabrairu da ya gabata, ya karbi umurnin sabon shugaban kasar na kafa wata sabuwar gwamnati nan take. Bayan shawarwari da ya yi tare da 'yan takara a cikin mako daya da ya gabata, Ibrahim Mahlab ya gabatarwa shugaban kasar Adly Mansour takardar jerin sunayen ministocinsa. Bisa labarin da kafar yada labarai a wurin ta bayar, an ce, takardar ba ta kunshi sunayen wasu manyan ministoci ba ciki hadda ministan tsaron kasar,don haka shugaba shi zai yanke shawara kan wannan abu.

An ba da labari cewa, sabuwar gwamnati tana kunshe da ministoci 31, biyar daga cikin su na rike da mukamai biyu, wato ministan matasa da na motsa jiki, ministan tsare tsare da na hadin kai da kasa da kasa, ministan masana'antu da na zuba jari da cikini, ministan ilmi da na nazarin kimiyya, ministan raya harkokin kasa da na raya yankunan kasa.

Mambobin sabuwar gwamnati a wannan karo babu babban sauyi idan aka kwatanta da wanda ya gabata. Bisa labarin da shafin yanar gizo na Internet na kasar ya bayar an ce, tsoffin ministoci 20 na mulkin Hazem Al-Beblawi sun zama sabbin ministocin sabuwar gwamnatin. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China