in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Masar sun baiwa Al-sisi hurumin shiga takarar zaben shugaban kasa
2014-01-28 09:55:08 cri
Babban kwamitin rundunar sojojin kasar Masar (CSFA) ya bada amincewarsa a ranar Litinin ga ministan tsaron kasar Masar, Abdel Fatah al-sisi, kuma shugaban rundunar sojojin kasar, don ya shiga takarar zaben shugaban kasar Masar a wani labarin da kamfanin dillancin labaran kasar MENA da shafin internet na Ahram suka bayar.

Haka kuma kwamitin ya amince da murabus din mista Al-sisi daga mukaminsa na shugaban rundunar sojojin kasar in ji MENA tare da cewa shugaban rundunar sojojin kasar zai yi bayani a cikin 'yan sa'o'i masu zuwa idan zai shiga takarar zaben shugaban kasar ko a'a. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China