in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron Masar zai iyar shiga takarar shugaban kasa idan al'ummar Masar ta nemi haka
2014-01-12 16:05:34 cri
Shugaban rundunar sojojin kasar Masar kana kuma ministan tsaron kasar Abdel-Fattah al-Sisi ya bayyana a ranar Asabar cewa zai iyar yin takarar zaben shugaban kasa idan har al'ummar kasar Masar ta bukaci haka sannan kuma idan ya samu amincewa daga wajen rundunar jojojin kasar, a cewar jaridar Al-Ahram a cikin shafinta na internet.

A yayin wani zaman taro da sojojin kasar suka shirya, mista Al-Sisi ya fada a gaban mahalarta taron cewa ba zai iyar juya baya ba ga kasar Masar.

Mista Al –Sisi ya yi amfani da wannan dama domin yin kira ga 'yan kasar Masar baki daya da su halarci zaben jin ra'ayi kan sabon kundin tsarin mulkin kasar da za'a shirya a ranakun 14 da 15 ga watan Janairu, tare da nuna cewa kundin na wakiltar kashi daya cikin kashi uku na sabon jadawalin tafiyar da mulkin kasar.

A karshe mista Al-Sisi ya nuna cewa idan har mutanen kasar Masar ba su harlarci wannan zaben raba gardama kan sabon kundin tsarin mulki sosai ba, to hakan zai kasance wani abun damuwa gare shi da kuma rundunar sojojin kasar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China