in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga mulkin wucin gadi cikin zaman lafiya a Masar
2014-01-15 12:26:51 cri

Babban sakatare na MDD, Ban Ki-moon dake mai da hankali kan zaben sabon kundin tsarin mulki a kasar Masar, ya yi kira a ranar Talata wajen ganin an gudanar da mulkin wucin gada cikin zaman lafiya a wannan babbar kasa dake arewacin Afrika, in ji kakakin Ban Ki-moon a cikin wata sanarwa. A cewar kakakinsa, Ban Ki-moon na jaddada muhimmancin giramama 'yancin gudanar da taron gangami da bayyana ra'ayi da kuma fatan ganin dukkan bangarorin da wannan rikicin siyasa ya shafa sun yi watsi karfin damtse domin koma wa teburin shawarwari.

Sakatare janar ya nuna goyon bayansa ga mutanen kasar Masar da su tabbatar da makomarsu kan wannan lokacin na wucin gadi cikin zaman lafiya da adalci, in ji wannan sanrawa. Tun ranar Talata har zuwa ranar yau Laraba, 'yan kasar Masar ke zaben raba gardama kan sabon kundin tsarin mulki. Masar ta dukufa wajen tafiyar mulkin wucin gadi bisa tsarin demokaradiyya tun faduwar shugaba Hosni Mubarak bayan boren 'yan kasar. A watan Yulin da ya gabata, rundunar sojojin kasar ta hambarar da shugaba Mohamed Morsi, suka dakatar kundin tsarin mulki, sannan suka kafa gwamnatin wucin gadi.

Mista Ban ya yi kira ga 'yan kasar Masar da su bayyana ra'ayinsu ta hanyar zaman lafiya, tare da nuna cewa, MDD za ta cigaba da tallafawa tsarin da 'yan kasar ke bi dake zuwa daidai da tsarin demokaradiyya wanda ke ba da damar fadin albakacin baki da 'yancin 'dan adam a cikin wannan kasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China