in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai harin boma-bomai a arewacin Masar
2013-12-24 18:30:04 cri
Tashar yanar gizo ta jaridar Al-Ahram ta Masar ta yi amfani da labarin ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar cewa, a safiyar yau talata 24 ga wata, an kai harin boma-bomai da aka dasa cikin mota a wani ginin ofishin 'yan sanda ta Daqahliya dake birnin Mansoura a arewacin kasar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 14, yayin da wasu 134 suka jikkata.

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai firaministan gwamnatin wucin gadi ta Masar, Hazem Beblawi ya ce makasudin wannan hari shi ne a tsorata fararen hula, tare da dasa shinge ga aikin gudanar da taswirar siyasa. Ya yi alkawarin kara kokari domin cafke wadanda suka tsara shirin da kuma gudanar da wannan danyen aiki. A sa'i daya, ya musunta cewa, gwamnatin wucin gadin kasar ta riga ta dauki kungiyar 'yan uwan Musulmi a matsayin kungiyar ta'addanci.

Kafin wannan, mai ba da shawara kan harkokin yada labaru na Hazem Beblawi, Sherif Shawky ya riga ya fidda sanarwar cewa, kungiyar 'yan uwan Musulmi kungiyar ta'addanci ce. Dadin dadawa, sanarwar ta kara da cewa, bayan haifar da rikicin zubar jini da lalata tsaron kasa, kungiyar ta fidda hakikanin fuskarta ta kungiyar ta'addanci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China