in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya kai ziyara a yankunan dake fama da talauci
2014-01-27 15:39:20 cri

Gabanin ranar bikin bazanar na gargajiyar kasar Sin, firaministan kasar Li Keqiang ya kai ziyara a lardin Shaanxi dake yammacin kasar Sin a ranar jiya Lahadi, domin ganawa da wasu mutanen dake fama da talauci, musammun ma tsoffin da ba su da muhallin zama da kananan yara marayu, inda ya yi alkawarin yin iyakacin kokarinsa domin tabbatar da mawadaciyar zaman rayuwa ga wadannan mutane, ta yadda kowa zai samu gida. Ya kara da cewa, bikin bazana na gargajiyar kasar Sin yana muhimmancin gaske ga Sinawa, wadanda suke dora babban muhimmanci kan zaman iyali da iyaye. Ya kamata, mu yi iyakacin kokarin ba da tabbaci ga zaman rayuwar jama'a, ba ma kawai mu kula da zaman rayuwarsu na da kullum ba, har ma mu kwantar da hankalinsu, kuma yin haka wata babbar kauna ce dake bayyana halayyar Sinawa ta asali, in ji mista Li Keqiang. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China