in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya gana da Ban Ki-Moon
2013-06-19 16:29:38 cri

Ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi ya gana da babban magatakardar MDD Ban Ki-Moon a ranar Laraban nan 19 ga wata a nan birnin Beijing.

A lokacin ganawar,Wang Yi ya nuna cewa, a matsayin wata kungiyar kasa da kasa mai fadi a ji, MDD tana taka wata muhimmiyar rawar da ba wanda zai maye gurbinta ba a cikin wasu batutuwan kasa da kasa kullum. Sin tana goya bayan MDD, kuma ta mai da tsarin dokokin MDD a matsayin ginshikin daidaita dangantakar dake tsakanin kasa da kasa, tare kuma da dukufa kan kiyaye zaman oda da doka na duniya bisa tsarin dokokin MDD.

A nasa bangare, Ban Ki-Moon ya ce, Sin tana taka rawar jagoranci cikin harkokin kasa da kasa gwargwadon karfinta, kuma ta ba da babbar gudunmawa wajen kiyaye zaman lafiya da tsaro, da samun bunkasuwa mai dorewa.

Don haka MDD ta nuna gare ta yabo kuma tana fatan Sin zata ci gaba da ba da taimako ga aikin kiyaye zaman lafiya da MDD ke gudanarwa, sa'anan su kara hadin gwiwa tsakaninsu don tinkarar kalubaloli ta kowane fanni tare. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China