in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan babban taron MDD kan kokarin samun dauwamammen ci gaba zai ba da sakwanni masu karfi cikin yakini a bayyane
2012-06-18 16:26:47 cri
A ran 18 ga wata, mataimakin ministan harkokin waje na Sin Xie Hangsheng ya bayyana cewa, Sin na fatan za a cimma matsaya daya a gun babban taron MDD kan kokarin samun dauwamammen ci gaba da za a yi daga ranar 20 zuwa ta 22 ga wata, a kokarin bayar da sakwanni masu karfi cikin yakini a bayyane domin farfado da hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a fannin kokarin samun ci gaba mai dorewa.

Mr. Xie wanda ya fadi haka a gun taron manema labaru na Sin da kasashen waje da ma'aikatar harkokin waje ta kasar ta shirya ,ya bayyana fatansa cewa, taron zai bi tunani da ka'idar Rio, musamman ma tsarin daukar nauyi daya amma da bambanci, a kokarin sa kaimi ga ra'ayoyin kasa da kasa na kara karfin siyasa, da tabbatar da yarjeniyoyin da aka kulla daga shekarar 1992 zuwa ta 2002 a dukkan fannoni, da tsara hakikanin shirin gudanarwa a bayyane, da kuma tabbatar da cika alkawarin wasu kasashen sukuni na ba da kudin agaji, da yin musayar fasahohi, da kara kwarewa da dai sauransu.

Ban da haka, Mr. Xie ya ce Sin na fatan babban taron zai zartas da wani bayanin sakamako mai inganci, a kokarin bayyana ra'ayoyin bangarori daban daban a fannin siyasa, da daidaita batutuwan da kasashe masu tasowa suke mai da hankali a kansu, a kokarin ba da jagoranci ga hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a nan gaba.

An ce, firaministan kasar Sin Wen Jiabao zai jagoranci kungiyar wakilan kasar don halartar taron, kuma zai yi muhimmin jawabi a gun taron. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China