in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da MDD abokan hadin gwiwa ne da suke samun ci gaba tare
2011-10-24 20:13:15 cri
Mr. Wu Hailong, mai ba da taimako ga ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a ran 24 ga wata a nan birnin Beijing, cewar kasar Sin da majalisar dinkin duniya abokan hadin gwiwa ne da suke samun ci gaba tare. Kasar Sin za ta ci gaba da kasancewa tamkar abokiyar M.D.D. a kokarin sanya M.D.D. ta kara taka muhimmiyar rawarta kan harkokin kasa da kasa.

A lokacin da ya gabatar da wani jawabi a yayin bikin murnar cika shekaru 66 da kafuwar majalisar dinkin duniya da aka shirya yau, Mr. Wu ya ce, a halin da ake ciki yanzu a duniya, batutuwan tsaron kai irin na gargajiya da wanda ba irin na gargajiya ba suna bullowa tare, ba ma kawai M.D.D. take da nauyin tabbatar da zaman lafiya a duniya ba, har ma tana da nauyin neman ci gaba da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa.

Sannan Wu Hailong ya nuna cewa, kasar Sin tana bukatar goyon baya daga wajen M.D.D. domin neman ci gaba, haka kuma, M.D.D. tana bukatar kasar Sin da ta kasance kan harkokin kasa da kasa, wannan zabi ne da aka yi bisa hanyar neman ci gaba da kasar Sin take bi. Kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan hanyoyin bude kofarta da yin hadin gwiwa da kuma neman ci gaba tare da sauran kasashen duniya ba. Kasar Sin ta zabi hanyar neman ci gaba cikin lumana ba zabi ne da ta yi a wani lokaci domin wani al'amari ba, wannan zabi ne da ta yi domin dacewa da zamani, da kuma kokarin bayar da karin gudummawarta wajen ci gaban wayin kai na kasa da kasa. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China