in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tayi kiran a ci gaba da kokarin yaki da ta'addanci a duniya
2013-05-11 15:48:48 cri
A ranar Juma'a wani babban jakadan kasar Sin ya nanata matsayin kasar Sin na kyamar ta'addanci inda yayi kira ga al'ummar duniya data ci gaba da hadin gwiwa da kwamitin sulhun MDD wajen yaki da ta'addanci.

Li Baodong, wanda shi ne wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD ya yi wannan kira ne yayin da yake jawabi a wajen wani taron kwamitin sulhun kan yaki da ta'addanci.

Li ya ci gaba da cewa kasar Sin na mai nuna kin amincewarta ga ta'addanci ta kowace fuska, bayan da shugabannin kananan kwamitocin kwamitin tsaron na MDD suka gabatar da jawabi kan batun.

Ya kara da cewa suna fata wadannan kwamitoci za su ci gaba da tattaunawa da kasashe mambobi, su kara inganta hadin gwiwa da sauran cibiyoyin MDD, kana a taimakawa kasashe mambobi musamman ma kasashe masu tasowa, domin a samu inganta aikin yaki da ta'addanci.

Jakadan na kasar Sin ya kuma jadadda cewa ko kadan kasar Sin bata amince da yin baki biyu ba kan yaki da ta'addanci. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China