logo

HAUSA

Labarin Bashir Umar Muhammed: Dan kasuwan Najeriya a kasar Sin (A)

2024-07-02 15:58:38 CMG Hausa

Bashir Umar Muhammed, haifaffen Kanon tarayyar Najeriya ne, wanda a yanzu haka yake gudanar da kasuwanci a kasar Sin.

A zantawarsa da Murtala Zhang, malam Bashir Umar ya bayyana yadda yake gudanar da harkokin kasuwanci a wasu kasashe, da dalilin da ya sa ya zo kasuwanci a kasar Sin.

Malam Bashir ya kuma bayyana yadda rayuwa da aikinsa yake kasancewa a kasar Sin, da wasu kalubaloli da yake fuskanta, da kuma yadda yake kokarin shawo kansu.

A shirin na makon gobe, za’a kawo muku ci gaban hirar da aka yi tsakanin Murtala Zhang da malam Bashir Muhammed. (Murtala Zhang)