logo

HAUSA

Mai fashin baki: Taron Amurka kan demokraddiya nuna girman kai ne
Rediyo
  • In Ba Ku Ba Gida
  • Sin da Afirka
  • Duniya A Yau
  • Wasannin Motsa Jiki
  • Allah Daya Gari Bambam
  • Nuryan Maimaiti: jerin kogunan Kezil sun samar da damar sa kaimi ga cudanya tsakanin kabilu daban daban na jihar Xinjiang

    Nuryan Maimaiti, wadda ta shafe shekaru 6 tana aikin binciken rukunin kogon Kezil, wadanda ke kasancewa kogon addinin Buddha da aka gada mafi tsufa, mafi girma, mafi dadewa, mafi yawan nau'o'in, kana mafi tasiri a Yankunan Yamma, wato wurin da ake kira da gama gari a jihar Xinjiang ta kasar Sin da tsakiyar Asiya, don gano tarihin mu'amala da cudanya tsakanin kabilu daban daban na jihar Xinjiang...

  • Sani Abdulkarim: Akwai damammaki da yawa a kasar Sin!

    Sani Abdulkarim, dan asalin jihar Kanon Najeriya ne, kuma malami daga jami’ar kimiyya da fasaha ta Wudil dake jihar Kano, wanda a yanzu haka yake karatun digiri na uku a wata jami’a dake nan birnin Beijing na kasar Sin, mai suna University of Science and Technology Beijing. A zantawarsa da Murtala Zhang, malam Sani ya bayyana ra’ayinsa kan ci gaban kasar Sin, da abubuwan da ya jawo hankalinsa a kasar, gami da bambancin yanayin karatu tsakanin gida Najeriya da Sin...

  • Yadda kasar Sin ke yunkurin bude kofa ga kasashen waje ta hanyar samar da hajoji da hidimomi masu inganci

    Duk da karuwar yunkurin kange tattalin arziki da kasashen yammancin duniya ke yi da kira da a raba gari da kasar Sin da babakere da danniya. kasar Sin ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta bude kofarta ga kasashen waje bisa matakai masu inganci don jawo jarin kasashen waje. Hakan ya sanya “taruka biyu” wato taron majalisar ba da shawara kan hankokin siyasa CPPCC da na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC da aka kammala ranakun 10 da 11 ga wata bi da bi, suka mai da hankali akan bude kofa ga kasashen wajen ta hanyar

  • Kalankuwar al’adun Afirka ta kayata gasar wasannin nahiyar da Ghana ke karbar bakunci

    Kalankuwar al’adun kasashen Afirka da aka gudanar, ta kayata gasar wasannin nahiyar karo na 13 da Ghana ke karbar bakunci. Yayin bikin bude gasar a birnin Accra a makon jiya, an gudanar da nune-nunen fasahohi da al’adun nahiyar ciki har da raye-raye, da kade-kade, da jerin gwanon masu nuna fasahohi, wadanda suka yi matukar nishadantar da ‘yan kallo.

  • Dabarun raya tattalin arziki sun yi amfani a kasar Sin

    A cikin shirin yau za mu duba wasu dabarun da gwamnatin kasar Sin ta dauka don raya tattalin arzikin kasar, musamman ma a fannonin habaka sayayya da kirkiro sabbin fasahohi.

LEADERSHIP