Kwamitin tsarin mulkin kasa na Chadi ya fitar da jerin sunayen ’yan takarar shugaban kasar
2024-03-25 09:56:31 CMG Hausa
Kwamitin tsarin mulkin kasa na kasar Chadi, ya fitar da jerin sunayen ’yan takarar shugaban kasar a jiya Lahadi, ciki har da shugaban gwamnatin rikon kwaryar kasar Mahamat Déby, da kuma firaministan kasar Succès Masra.
Za a gudanar da babban zaben kasar Chadin ne a ranar 6 ga watan Mayu. (Safiyah Ma)