logo

HAUSA

Xi Jinping ya jaddada bukatar bunkasa ci gaba mai inganci a bangaren hada-hadar kudi na kasar

2024-01-16 20:20:27 CMG Hausa

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar dagewa a kan hanyar raya bangaren hada-hadar kudi mai sigar musammam ta kasar Sin da kuma inganta bunkasa ci gaban bangaren.

Xi Jinping ya bayyana haka ne yau, yayin bude wani zaman nazari a kwalejin horar da jami’an JKS na kwamitin kolin jam’iyyar. (Fa’iza Mustapha)