Adadin wadanda suka mutu sakamakon gobarar daji a Aljeriya ya kai 34
2023-07-25 10:57:05 CMG Hausa
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Aljeriya ta sanar a ranar Litinin cewa, adadin wadanda suka mutu sakamakon gobarar daji a arewacin kasar Algeria ya karu zuwa 34, ciki har da sojoji 10.
Ma'aikatar ta ce kimanin mutane 8,000 ne ke yaki da gobarar a larduna 11, da manyan motoci 529 da kuma jirage masu saukar ungulu na kashe gobara da dama.
Gobarar ta tashi ne da daddare a ranar Lahadi musamman a lardunan Bejaia, Jijel, da Bouira, amma cikin sauri ta bazu saboda iska mai karfin gaske, inda ta yi barna sosai. (Yahaya Babs)