Matsalar jin kai da ’yancin ’yan gudun hijira a tsakiyar rangadin shugaban CNDH a Agadez
2023-07-16 15:26:05 CMG HAUSA
Shugaban kwamitin kare hakkin dan adam na kasa CNDH, Maty Elhadji Moussa ya fara ziyarar aiki tun daga ranar 12 ga watan Julin shekarar 2023 a yankin Agadez. Rangadin shugaban CNDH na da burin sanin halin jin kai da yancin ’yan gudun hijira a yankin Agadez, tare da taimakon kungiyar kula da ’yan gudun hijira ta MDD wato OIM.
Daga birnin Yamai, abokin aikin mu Mamane Ada ya turo mana da wannan rahoto