Ruwa da iska mai karfi sun lalata muhallin magidanta kusan sama da 200 a jihar Kebbi
2023-07-03 08:56:27 CMG HAUSA
Magidanta fiye da 200 aka yi hasashen sun rasa muhallan su sanadiyar ruwan sama da iska mai karfi a kauyen Zauro dake yankin karamar hukumar Mulki ta birnin Kebbi dake jihar Kebbi a arewacin Najeriya.
Al’amarin ya faru ne a karshen makon jiya cikin dare lamarin da ya sanya iyalai da dama kwanan zaune sakamakon rashin makwaci.
Daga tarayyar Najeriya Wakilin mu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.