Shugaba Xi ya halarci tattaunawa tare da walikan NPC na Mongolia ta Gida
2022-03-05 17:22:01 CRI
Da yammacin yau Asabar, shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban kwamitin tsakiya na aikin soja na JKS Xi Jinping, ya halarci tattaunawa tare da walikan majalisar wakilan jama’a ta kasar ta NPC daga jihar Mongolia ta Gida.
Shugaban tare da wakilan, sun tattauna muhimman batutuwa, a wani bangare na zaman shekara-shekara karo na 5, na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta NPC ta 13. (Saminu)