in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi ganawa tsakanin manyan jami'an kasashen Sin da na Kongo Brazzaville
2013-06-26 11:16:07 cri

Yau Laraba 26 ga wata, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Yu Zhengsheng ya gana da shugaban kwamitin kula da harkokin tattalin arziki da al'umma na kasar Kongo Brazzaville Jean-Marie Tassoua a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Yu Zhengsheng ya nuna cewa, a shekarun baya, kasashen biyu sun samu saurin bunkasuwar dangantakar dake tsakaninsu. Sin na fatan hadin kai da kasashen Afrika ciki hadda Kongo Brazzaville, domin yin amfani da zarafi mai kyau wajen habaka hadin gwiwa a tsakaninsu, da kara zurfafa zumuncin dake tsakaninsu. Ban da haka, kasar Sin na fatan kasashen biyu za su kara tuntubar juna ta fuskar tattalin arziki da al'umma ta hanyoyi daban-daban a dukkan fannoni, a kokarin sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar sada zumunci a tsakaninsu.

A na shi bangaren, Jean-Marie Tassoua ya ce, kwamitinsa zai ta hada kai da kasar Sin domin ba da gudummawa wajen zurfafa dangantakar dake tsakaninsu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin ya gana da shugaban majalisar tattalin arziki da al'ummar Mauritaniya 2013-04-26 16:29:24
v An shigar da lambun shan iska na Sangha cikin takardar jerin sunayen kayayyakin gargajiya na kasa da kasa 2012-07-11 15:24:49
v MDD ta soki lamarin kai hare hare kan sojojinta a RDC 2012-07-07 16:39:45
v Kasar Togo ta bayar da agajin abinci da magunguna ga wadanda  fashewar makamai ta rutsa da su a kasar Congo Brazzaville 2012-03-13 11:27:33
v Gwamnatin Kongo (Brazzaville) ta shirya bikin jana'izar mutanen da suka kwanta dama a sakamakon fashewar ginin ajiyar makamai 2012-03-12 15:00:26
v Kungiyar ba da agaji ta Red Cross ta himmatu wajen bada taimako ga wadanda fashewar albarusai na Brazzaville ya rutsa da su 2012-03-10 17:07:47
v Gwamnatin kasar Kongo Brazzaville ta tsaida kudurin gudanar da bikin jana'izar mutanen da suka mutu a sakamakon fashewar bama bamai 2012-03-09 10:38:12
v Mutane 300 sun mutu sakamakon tarwatsewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai a Congo (Brazzaville) 2012-03-07 13:39:33
v Ban Ki-Moon ya nuna rashin jin dadi kan fashewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai na kasar Congo Brazzaville 2012-03-06 14:40:19
v Mutane a kalla 200 sun mutu sakamakon wata fashewa a wani dakin ajiye makamai a kasar Kongo Brazzaville 2012-03-05 11:28:18
v Za'a bude taro na 22 na ministocin kasashen Tsakiyar Afirka a birnin Brazzaville 2011-12-08 15:20:14
v Ana jiran sakamakon shari'ar da aka gudanar kan wasu maharba guda 2 a kasar Kongo Brazaville 2011-12-08 15:18:13
v Yanayi na kyautatuwa ta fuskar siyasa a kasar Congo-Braza 2011-09-20 11:03:26
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China