in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya nuna rashin jin dadi kan fashewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai na kasar Congo Brazzaville
2012-03-06 14:40:19 cri

A madadin babban sakataren MDD Ban Ki-Moon, kakakinsa ya bayar da sanarwa a ranar 5 ga wata, inda ya nuna rashin jin dadi kan batun fashewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai a ranar 4 ga wata a garin Brazzaville, babban birnin kasar Congo.

A cikin sanarwar, Ban Ki-Moon ya bayyana cewa, a yayin da ake fama da wannan wahala, MDD za ta ci gaba da ba da taimakon jin kai da gudanar da aikin ceto.

Bisa labarin da aka bayar, batun fashewar bama-bamai a dakin ajijar makamai da ta abuku a garin Brazzaville, babban birnin kasar Congo,fashewar bama-baman ta yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 146, a yayin da wasu fiye da dubu daya suka ji rauni, daga cikin mamatan, akwai ma'aikata Sinawa guda 6.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China