in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 300 sun mutu sakamakon tarwatsewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai a Congo (Brazzaville)
2012-03-07 13:39:33 cri

Adadin mutanen da suka mutu a sanadiyyar tarwatsewar bama-bamai a dakin ajiyar makamai da ke Brazzaville, babban birnin kasar Congo (Brazzaville) ya kai 300, kamar yadda fadar shugaban kasar ta sanar a yammacin ranar Talata 6 ga wata. A ran nan kuma, kakakin gwamnatin kasar ya sanar da cewa, tun daga wannan rana, a duk kasar za a yi zaman ta'aziyya ga wadanda suka rasu sakamakon tarwatsewar bama-baman.

Sama da mutane 1500 ne suka samu rauni a cikin wannan lamari kamar yadda alkaluma daga bangaren asibitocin Brazzaville suka tabbatar. Emilienne Raoul, ministan kula da harkokin al'ummar da lamuran jin kai da agaji na kasar ya sanar da manema labarai cewa, gwamnatin ta girka wani sansanin da zai dauki mutane 5000 da suka kasance ba su da muhalli, suna kuma bukatar kayayyakin masarufi da magungunan kariya daga cutar zazzabin malariya, zawo da mura.

Emilienne Raoul ya kuma yi kira zuwa ga al'umma da ta kawo taimako ga wadanda ba su da muhalli.

Kafin wannan kuma, bisa adadin da dakunan ajiyar gawawwakin da ke Brazzaville ya sanar, an ce, a kalla mutane 215 ne suka rasa rayukansu a sakamakon tarwatsewar bama-baman.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China