in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Kongo Brazzaville ta tsaida kudurin gudanar da bikin jana'izar mutanen da suka mutu a sakamakon fashewar bama bamai
2012-03-09 10:38:12 cri
A ran 8 ga wata, gwamnatin kasar Kongo Brazzaville ta gudanar da taron ministoci, inda ta tsaida kudurin cewa, ranar 11 ga wata a zauren majalisar dokokin kasar dake Brazzaville, babban birnin kasar, za a gudanar da bikin jana'izar mutanen da suka mutu a sakamakon fashewar bama bamai da ta faru a dakin ajiye makamai na birnin a ran 4 ga wata, kuma shugaban kasar Denis Sassou Nguesso zai halarci bikin.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, gwamnatin kasar za ta bada kudin taimako a kalla dala dubu 6 ga kowane iyali da wannan hadari yayi wa tasiri.

Ban da wannan kuma, ministan kula da tattalin arziki da manufofi da yankunan kasar Kongo Brazzaville Pierre Moussa ya sanar a ran 8 ga wata cewa, kasarsa za ta gina gidaje dubu 5 ga mutanen da gidajensu suka lalace a sakamakon hadarin.

Kana Moussa ya ce, ya zuwa yanzu, yawan 'yan gudun hijira na wannan bala'i a kasar ya kai 13854, kuma yawan mutanen da suka ji rauni da aka yi rajista a hukumomin likotoci na birnin Brazzaville ya kai 2315. Ban da wannan kuma, bisa labarin da kwamitin kula da aikin bada jinya bayan fashewar ya sanar cewa, ya zuwa ranar 8 ga wata, mutane kimanin dubu 1 suka sami sauki da barin asibitoci bayan da aka yi musu jinya.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China