in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yanayi na kyautatuwa ta fuskar siyasa a kasar Congo-Braza
2011-09-20 11:03:26 cri
Ministan harkokin wajen kasar Congo-Braza, Basile Ikouebe da sakatare janar na MDD mista Ban Ki-moon sun yi sharwarwari tare, inda suka bayyana gamsuwarsu a ranar Lahadi a birnin New york kan halin da kasar Congo ke ciki na zaman jituwar al'umma da na siyasa.

A cewar wani rohoto na tawagar dindindin ta kasar Congo dake MDD da aka baiwa manema labarai, manyan mutanen biyu sun nuna jin dadinsu a fili a yayin wata ganawa ta bangarorin biyu a gabanin zaman taron MDD karo na 66, wanda a yayin ganawar suka tattauna halin kasar Congo, a wannan yanki, a nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

A game da jamhuriyar kasar Congo, mutanen biyu sun nuna yabo kan yadda aka gudanar a kasa da kasa na Afrika game da harkokin internet, da dunkulewar kasa mai yanci, niyyar mai dorewa ta kasar Congo wajen kare hakkin bil'adam a duk fadin kasar da ma duniya, musammun ma a matsayinta ta mambar kwamitin kare hakkin dan adam a MDD, da wanzar da tsarin demokaradiya, rohoton ya kara da cewa.

Game da wannan yanki da ma duniya, mista Ikouele da Ban Ki-moon sun tabo batutuwan da suka shafi tsaron Afrika ta tsakiya, da duniya tare da tabo batun kawo sauye sauye a MDD. Haka sun yi shawarwari kan halin da kasar Libya ke ciki a gabanin wani babban taro da majalisar zata gudanar a ranar Talata a birnin New York. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China