A watan Maris na shekarar 2011, an barkar da rikicin Syria. A cikin shekarun 12 da suka gabata, kasar Amurka na ci gaba da kai dauki daga dakarun soji da saka haramtattun takunkumi ta gaban kai ga Syria, lamarin da ya haddasa bala'o'in jin kai masu yawa. An tilastawa jama’ar kasar da dama tserewa daga gidajensu, kuma iyalin Hussein el Jadoua’a sun yi tattaki zuwa kasar Lebanon dake makwabtaka.
Ibrahim Bature, dan asalin jihar Katsina ta arewacin Najeriya ne, wanda a yanzu haka yake karatun digiri na uku a sashin nazarin ilimin kiwon dabbobi, da magungunan dabbobi na Lanzhou na cibiyar binciken kimiyyar ayyukan gona ta kasar Sin. A wata zantawar da ya yi da Murtala Zhang, malam Ibrahim Bature ya bayyana ci gaban kasar Sin a idanun sa, da ra’ayin sa kan muhimmancin inganta hadin-gwiwa tsakanin kasar sa wato Najeriya da kasar Sin......
A bana ne ake cika shekaru 20, da Amurka da kawayenta suka kaddamar da yaki a kasar Iraki, ba tare da samun izini daga MMD ba, bisa hujjar cewa, ta gano makaman kare-dangi a kasar ta Iraki. Amma daga baya, an tabbatar da cewa, Iraki ba ta da irin wadannan makamai. Wannan ya kara tabbatar da zalunci da nuna fin karfi da Amurka ke nunawa kan wasu kasashe.
A kwanan baya, shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum ya jagoranci wani zaman taro na manyan jami ai kan zuba a fannin wasannin motsa jiki musammun ma game da wasan kwallon kafa a fadar shugaban kasa dake birnin Yamai, ganin yadda kasar Nijar take kokarin kama hanya a bangaren wasan tama’ula da ma sauran wasannin motsa jiki a dandalin kasa da kasa.
A yayin babban taron tattaunawa tsakanin Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin da jam'iyyun siyasa na duniya da aka gudanar ta kafar internet a kwanakin baya, shugaban kasar Sin Xi jinping ya gabatar da shawarar wayewar kai ta duniya. A cikin shirinmu na yau za mu saurari ra'ayin wani shahararren shehun malami dan kasar Mali dangane da wannan shawara, gami da rawar da jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ke takawa a duniya.