06-Mar-2026
05-Mar-2026
03-Mar-2026
20260306-Yamai
00:00
1x
A daidai lokacin da aka kashe wutar gasar wasannin Olympics ta Milan-Cortina ta lokacin hunturun bana, shi ma “gidan kasar Sin” ya kammala nune-nune da ya tsara gudanarwa ga al’ummun duniya. Cikin kwanaki 19 yana gudanar da ayyuka, gidan wanda ya kasance dandalin na musamman, wanda ya gudana karkashin kwamitin shirya gasar Olympic na kasar Sin, ya taimaka matuka ga tawagar kasar Sin mai halartar gasar, inda baya ga zama cibiyar tsare-tsare, ya kuma kasance cibiyar nuna al’adun kasar Sin ga masu ziyara na sassan kasa da kasa.
Yayin da jiragen yakin Amurka da Isra'ila ke ci gaba da kai hare-hare a Iran, ita ma Iran ta ci gaba da mayar da martani kan sansanonin sojin Amurka na Gabas ta Tsakiya da kuma kasar Isra'ila, lamarin da ya janyo mafi yawan yankin ya shiga wani yanayi mai hatsarin gaske na daukar fansa. Daga Beirut zuwa Dubai, daga Kuwait zuwa Qatar, fararen hula na fuskantar karuwar asarar rayuka, da fuskantar cikas ga rayuwar yau da kullum musamman ma bisa yadda lamarin ke faruwa a cikin watan azumin Ramadan da al’ummar galibin kasashe Gabas ta Tsakiya ke bukatar kyautatuwar rayuwa saboda azumi, kana ana fuskantar tsananin rashin tabbas game da abin da zai iya biyo baya.
02-Mar-2026
28-Feb-2026
27-Feb-2026
Huang Lili da Kang Zhensheng, ma’aurata ne, kuma malamai ne a jami’ar koyar da ilmin aikin gona da na gandun daji da ake kira da Northwest Agriculture & Forestry University (NWAFU), dake lardin Shaanxi na arewa maso yammacin kasar Sin. Ko da yaushe tabbatar da cewa kasar Sin ta tsaya da kafarta wajen samar da abinci ya kasance burinsu ne.