18-Aug-2026
17-Aug-2026
15-Aug-2026
13-Aug-2026
20260818-Yamai
00:00
1x
Dr. Musa Abubakar Tadda, dan asalin jihar Kano ne a tarayyar Najeriya kuma mai bincike mai zurfi a fannin fasahar noma, inganta muhalli, da kuma makamashi a birnin Hangzhou na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, Dr. Musa Tadda wanda ya shigo kasar Sin tun shekara ta 2017, ya bayyana ra’ayinsa kan yanayin rayuwa da karatu a kasar Sin, da kuma burin da yake son cimmawa bisa karatun da ya yi a kasar...
A cikin shirinmu da ya gabata, mun saka muku hirar da wakiliyarmu Fa’iza Muhammad Mustapha ta yi da sabon jakadan Najeriya a kasar Sin, Abdulrahman Dambazau, game da nasarorin da aka samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Najeriya tun bayan kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu. Kuma a cikin shirinmu na wannan mako, za mu saka muku ragowar tattaunawarsu, wadda ta shafi wasu fannoni uku, wato musayar al’adu da cudanyar jama’a, da kuma fa’idojin manufofin Sin ga Afirka, gami da tsare-tsaren ci gaban kasashen biyu da kuma makomar hadin gwiwarsu a nan gaba, musamman ma kan ci gaban abokantaka tsakanin Sin da Najeriya.
04-Aug-2026
28-Jul-2026
16-Aug-2026
11-Aug-2026
“Na zo Chengdu don ganin manyan dabbobin Panda, kuma sai na zauna saboda mutanen birnin da kuma harkokin wasanni,” cewar Lamia Arab wadda ta zo Sin daga birnin London na Birtaniya. Ta je Chengdu, babban birnin lardin Sichuan ne a 2017. Yanzu malama ce a jami’ar Chengdu. Wasanni sun zama tamkar fasfonta yayin zama a Chengdu, al’ada kuma ta zama abun da ya zaunar da ita a birnin. A ganinta, Chengdu ba waje ne mai hada-hada ba kadai, misali ne na wurin da ya hada wasanni da al’adu, kuma inda gargajiya da zamani suka hade da juna.