02-Sep-2026
01-Sep-2026
31-Aug-2026
28-Aug-2026
27-Aug-2026
20260902-Yamai
00:00
1x
Shirinmu na makon nan, ya duba yadda harkar fina-finai a kasar Sin ta kasance a lokacin hutun zafi na bana, inda kudaden da aka samu daga gidajen kallon fina-finai suka karu idan aka kwatanta da bara. Ko da yake sakamakon bana bai kai matsayin wanda aka samu a shekarar 2023 ba, wanda ya kafa tarihi, masana sun ce yawan nau’o’in fina-finan da aka samar a bana, da kuma ingancinsu, na daga cikin abubuwan da suka sanya wannan kakar ta kasance mai armashi.
A gundumar Dulongjiang da ke cikin tsaunuka, da kwarurruka masu zurfi a karkashin lardin Yunnan na kan iyakar kudu maso yammacin kasar Sin, inda al’ummar kabilar Dulong suke rayuwa, wata mace ’yar kabilar mai suna Li Yuhua tana da sanannen lakabi na “Mai kula da gandun daji na Bakan Gizo.” A cikin shekaru tara da suka wuce, ta rika yin sintiri da kafa a cikin dazuzzukan da ba a sare su ba, domin kiyaye albarkatun dabbobi, da tsirrai da ba a saba gani ba a yankin kan iyaka. A lokaci guda kuma, tana kokarin bincike, tare da farfado da fasahar sana’ar hannu ta gargajiya da al’ummarta suka gada tun shekaru dubu, kana ta jagoranci kafa kungiyar mata ta taimakon juna, wadda ke ba daruruwan mata a tsaunuka damar samun kudin shiga mai dorewa ta hanyar kwarewarsu. Labarinta ya nuna a fili yadda mata daga kananan kabilu a yankunan kan iyaka na kasar Sin ke fita daga talauci, tare da daidaita tsakanin kiyaye muhalli da samun karin kudin shiga tare.
Saifullahi Yusuf Zurmi, dan jihar Zamfara ne na tarayyar Najeriya, wanda ya shigo kasar Sin kwanan nan don halartar wani taron kara wa juna sani na wasu kwanaki. Kafin ya kammala ziyararsa wannan karo a kasar Sin, Murtala Zhang ya samu damar zantawa da shi, inda ya bayyana wasu abubuwa da ya karu da su game da kasar, ko a fannin aiki, ko kuma a fannin al’adu da dabi’un mutanen kasar. Malam Saifullahi ya kuma bayyan wasu abubuwan ci gaban kasar Sin da suka burge shi, gami da fatansa da kira ga...
04-Aug-2026
28-Jul-2026
26-Aug-2026