in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Namibia ya lashe zaben shugabancin jam'iyya mai mulkin kasa
2017-11-28 09:46:39 cri
Bisa labarin da aka samu a jiya Litinin, an ce, jam'iyya mai mulkin kasar Namibia wato SWAPO, ta fidda sanarwa a safiyar ranar 27 ga wata a birnin Windheok, fadar mulkin kasa cewa, shugaba mai ci Hage Geingob ya lashe zaben shugaban jam'iyyar da aka gudanar a karshen makon da ya gabata.

An kira cikakken zaman taron wakilan jam'iyyar SWAPO karo na shida a birnin Windheok, a tsakanin ranar 23 zuwa ranar 26 ga watan nan da muke ciki, inda aka zabi sabon shugaban jam'iyyar, da kuma mataimakinsa da dai sauran jami'an jam'iyyar.

Kaza lika mataimakin firaministan kasar na yanzu, kana ministan dake kula da harkokin dangantakar diflomasiyya da hadin gwiwar kasa da kasa Netumbo Nandi Ndaitwah, shi ne ya lashe zaben mataimakin shugaban jam'iyyar ta SWAPO mai mulkin kasar ta Namibia. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China