in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Namibia: Za a bude makarantar kyautata tunanin al'umma
2016-05-23 09:45:25 cri
Jam'iyyar Swapo dake mulki a Namibia, ta shirya kaddamar da wata makaranta ta musamman, wadda za ta maida hankali ga kyautata tunanin 'yan kasar, a wani mataki na inganta da'a da kishin kasa.

Sakataren jam'iyyar na kasa Nangolo Mbumba ne ya bayyana hakan a jiya Lahadi, yana mai cewa daukar wannan mataki zai baiwa matasa damar zama masu kyawawan halaye. kazalika makarantar za ta rika koyar da darussan tarihin kasar, da fayyace manufofin jam'iyyar ta Swapo, ta yadda hakan zai bada damar samun magada a jam'iyyar bayan shudewar wadanda ke rike da ita a yanzu.

A bara mai dai jami'in jam'iyyar mai kula da harkokin yada bayanai Helmut Angula, ya bayyana burin da Swapon ke da shi, na samar da jagorori da za su iya wakiltar jam'iyyar bisa kwarewa, tare da nuna kyakkyawan misali.

Jam'iyyar Swapo ce dai ke mulkin Namibia, tun bayan samun 'yancin kan kasar a shekara ta 1990. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China