in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadduran mota sun yi sanadin mutuwar mutane casa'in da hudu yayin bukukuwan karshen shekara a kasar Namibia
2017-01-06 13:36:40 cri
A cewar asusun kula da wadanda hadarin mota ya rutsa da su na kasar Namibia, mutane casa'in da hudu ne suka mutu tun bayan kaddamar da gangamin kiyaye haddura a lokacin bukuwan karshen shekara, daga ranar 22 ga watan Nuwamban 2016 zuwa 2 ga watan nan da muke ciki.

Wata sanarwa da asusun ya fitar ta ce, mutane dari takwas da casa'in da hudu ne suka jikkata sanadiyyar haddura dari hudu da tamanin da suka auku a kan titunan fadin kasar. Adadin ya ragu idan aka kwatanta da na bara da mutane dubu daya da sittin da biyu suka jikkata sanadiyyar haddura dari biyar da talatin.

Adadin wadanda suka rasa rayukansu kuwa ya ragu ne da guda daya, inda a bara aka samu mutuwar mutane casa'in da hudu.

A kokorin sake rage aukuwar haddura a bana yayin da ake kokarin komawa makaranta da kuma aiki a kasar, asusun ya sanar da cewa zai fara aiki a wasu titunan kasar domin tabbatar da matafiya sun isa inda suke son zuwa lami lafiya. (Fa''iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China