in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardan MDD ya nuna damuwa kan kada kuri'un neman 'yancin kai a yankin Kurdawa na Iraki
2017-09-26 13:32:23 cri
A jiya Litinin ne, babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya fidda wata sanarwa ta bakin kakakinsa, inda ya nuna damuwa kan yadda al'ummar yankin Kurdawa suka kada kuri'ar neman 'yancin cin gashin kai, yana mai cewa, lamarin zai iya haddasa tashe-tashen hankula a yankin.

Mr. Guterres ya ce, ana mutunta 'yancin kasar Iraki, don haka, ya kamata a warware sabanin dake tsakanin gwamnatin tsakiyar kasar Iraki da gwamnatin yankin Kurdawa ta hanyar siyasa.

Ya kuma nuna fatan cewa, lamarin ba zai haifar da illa ga MDD wajen gudanar da ayyukanta a yankin Kurdawa ba, a sa'i daya kuma, ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ci gaba da nuna goyon baya ga MDD wajen gudanar da ayyukanta a kasar yadda ya kamata.

A jiya Litinin ne, Kurdawan Iraki sun kada kuri'un neman 'yancin cin gashin kan yankinsu, lamarin da ya gamu da rashin amincewa kwarai da gaske daga gwamnatocin Iraki da Turkiya da kuma Iran.

Bugu da kari, kasar Amurka da kungiyar tarayyar kasashen Turai sun nuna goyon bayansa kan dunkulewar kasar Iraki baki daya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China