in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin zata samar da kayan tallafin jinkai ga Iraqi
2017-07-27 11:31:29 cri
Kasar Sin zata samar da tallafin jinkai ga kasar Iraqi, kamar yadda aka ambata karkashin wata yarjejeniayar fahimtar juna da aka kulla a birnin Bagadaza a ranar Laraba.

Jakadan Sin Chen Weiqing, da ministan cikin gidan Iraqi Qasim al-Araji, ne suka jagoranci bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar a madadin kasashen biyu.

Tallafin wanda kasar Sin zata samar, zai taimaka wajen aiwatar da shirin bada kayayyakin jinkai a kasar Iraqin.

Chen Weiqing ya taya gwamnatin Iraqi murna bisa nasarar data cimma a yaki da ta'addanci, kana yace gwamnatin Sin zata cigaba da karfafa gwiwa ga kamfanonin kasar Sin dasu shiga aikin gine ginen farfado da kasar Iraqin bayan yaki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China