in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Iraqi sun kashe dakaru kungiyar IS 66
2017-08-20 13:18:33 cri
Jiya Asabar 19 ga wata, rundunar sojojin kasar Iraq ta sanar da cewa, sojojin gwamnatin kasar sun kashe dakarun kungiyar IS 66, a yayin da suka gudanar da aikin tarwatsa wani sansanin kungiyar dake yammacin birnin Mosul na kasar.

Kuma cikin sanarwar da ta fitar, ba ta ambaci daidai lokacin da ta gudanar da wannan aiki ba.

A ranar 10 ga watan Yuli, rundunar sojojin gwamnatin kasar Iraq ta kwace ikon birnin Mosul, fadar mulkin lardin Ninewa, wanda yake da nisan kilomita dari 4 daga birnin Bagadaza, babban birnin kasar Iraqi. A watan Yunin shekarar 2014, kungiyar IS ta mamaye birnin Mosul, sa'an nan, kungiyar ta mai da birnin babban sansaninta mafi girma a duk fadin kasar ta Iraqi.

A halin yanzu, sojojin kasar Iraqi suna taruwa a yankin dake yammacin birnin Mosul, domin shiryawa game da farmakin da za su kaddamar domin kwace ikon birnin Tal Afar. Birnin Tal Afar, yana yammacin birnin Mosul, wanda yake da nisan kilomita 70 daga birnin, kuma shi ne sansani na karshe na kungiyar IS dake cikin lardin Ninewa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China