in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin yankin Kurdistan na kasar Iraki ta sanar da kada kuri'un jin ra'ayoyin jama'a bisa shirin da aka tsara
2017-09-24 13:26:35 cri
Gwamnatin yankin Kurdistan na kasar Iraki ta musunta labarin da aka bayar na cewa za'a jinkirta kada kuri'ar jin ra'ayoyin jama'a kan samun 'yancin kan yankin a jiya 23 ga wata, ta jaddada cewa, za a kada kuri'un bisa shirin da aka tsara wato a gudanar da shi a ranar 25 ga wannan wata.

Gidan telabijin na kasar Iraki ya ambato kalaman babban jami'in jam'iyyar kawancen Kurdistan Pavel Talabani yana cewa, bayan da manyan jam'iyyun yankin suka yi bincike kan dukkan shawarwarin da aka basu, shawarar jinkirta kada kuri'ar da kasar Amurka da Birtaniya da sauran kasashe da kuma MDD suka bayar ta fi dacewa ga jama'ar Kurdistan.

Game da wannan batu, wani jami'in ofishin shugaban yankin Kurdistan ya bayyana cewa, maganar Talabani ra'ayi ne na kashin kansa, bai wakilci ra'ayin gwamnatin yankin ba, za a kada kuri'un bisa shirin da aka tsara.

Da ma,gwamnatin yankin Kurdistan da gwamnatin tsakiya ta kasar Iraki babu kyakkyawar hulda a tsakaninsu, bangarorin biyu suna da matsaloli kan mallakar yankuna da dama, musamman jihar Kirkuk dake da albarkatun man fetur. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China