in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya halarci taron ganawar shugabannin kasar Sin da kungiyar EU karo na 19
2017-06-03 13:03:09 cri
Jiya da safe ne, firaministan kasar Sin Li Keqiang da shugaban majalisar Turai Donald Tusk da kuma shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Turai ta EU Jean - Claude Juncker suka jagoranci taron ganawar shugabannin kasar Sin da kungiyar EU karo na 19, wanda aka yi a hedkwatar majalisar zartarwar kungiyar Turai dake birnin Brussels na kasar Belgium.

A yayin taron, Li Keqiang ya bayyana cewa, cikin 'yan shekarun nan, ana ci gaba da samun ci gaban hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da bangaren Turai, inda suka dukufa wajen aiwatar da yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris domin karfafa hadin gwiwar bangarorin biyu wajen fuskantar sauyin yanayin duniya. Haka kuma, sun dukufa wajen aiwatar da jadawalin samun dauwamammen ci gaba nan da shekarar 2030, da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin yaki da ta'addanci da kuma kiyaye tsaro.

Bugu da kari, Li Keqiang ya jaddada cewa, bisa yarjejeniyar da aka kulla kan shigar da kasar Sin cikin kungiyar cinikayya ta duniya ta WTO, ya kamata bangarorin da abin ya shafa su aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata, ganin cewa nauyi ne dake kansu, da kuma ka'idojin kasa da kasa da ya kamata a martaba. Haka zalika, za a iya warware sabanin dake tsakanin kasar Sin da bangaren Turai ta hanyar yin shawarwari a tsakanin bangarorin biyu, ko kuma a tsakanin bangarori daban daban da abin ya shafa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China