in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da tattaunawa kan manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da EU zagaye na 7
2017-04-20 15:11:48 cri
An gudanar da tattaunawa game da manyan tsare-tsare a tsakanin bangaren kasar Sin da na kungiyar tarayar turai ta EU zagaye na 7 a jiya Alhamis a nan birnin Beijing, inda mamban majalissar zartaswar kasar Sin Yang Jiechi, da babbar wakiliyar kungiyar EU mai kula da harkokin waje da manufofin tsaro, kuma mataimakiyar shugabar kwamitin kungiyar EU Federica Mogherini suka shugabanci ganawar tare.

A yayin tattaunawar, bangarorin biyu sun amince da kara bunkasa mu'ammala da juna, game da batutuwan duniya, da ci gaba da sa kaimi ga kyautata tsarin tafiyar da harkokin duniya, da bunkasar kasashe bisa daidaito mai dorewa.

Bangarorin biyu sun ce za su ci gaba da kokari tare, don sa kaimi ga samun sabon ci gaba, a yayin taron koli na kungiyar G20 da zai gudana a birnin Hamburg, bisa tushen taron kolin kungiyar na Hangzhou. Kaza lika bangarorin biyu sun amince da sa kaimi ga aiwatar da yarjejeniyar Paris ta sauyin yanayi, da ajandar samun bunkasuwa mai dorewa nan da shekarar 2030, da kuma fadada hadin gwiwarsu a fannin kiyaye tsaro.

Har wa yau, bangarorin biyu sun yi musayar ra'ayoyi kan batutuwan kasa da kasa, da na yankuna, ciki har da batun Syria, da na nukiliyar Iran, da yanayin da ake ciki a zirin Koriya da sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China