in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta jaddada goyon bayanta ga dunkulewar Turai
2017-06-01 09:52:12 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya jaddada manufar kasar Sin ta goyon bayan dunkulewar kasashen Turai. Mr. Li ya bayyana hakan ne yayin ganawar sa da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel a birnin Berlin, yayin taron shekara shekara da jagororin kasashen biyu ke gudanarwa tsakanin su tun daga shekarar 2004.

Ya ce, Sin na fatan yin hadin gwiwa da kungiyar tarayyar Turai ta EU, wajen ganin an samu karfi na sarrafa al'amuran duniya a sassa daban daban, tare da fadadar tattalin arzikin duniya a yankuna da dama.

Birnin Berlin ne zangon farko da firaministan na kasar Sin ya sauka, cikin ziyarar aiki ta kwanaki 3 da zai gudanar a Jamus da kasar Belgium.

A birnin Brussels, Li Keqiang zai jagoranci taro na 19, na Sin da kasashen Turai tare da shugaban kungiyar EU Donald Tusk, da jagoran hukumar gudanarwar kungiyar ta Turai Jean-Claude Juncker.

Kaza lika zai gana da shugabannin kasar Belgium kafin dawowa kasar Sin.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China