in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasa da kasa sun yaba jawabin da Xi Jinping ya yi a birnin Geneva
2017-01-20 11:28:45 cri
A ranar 18 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci babban taron inganta makomar bil Adama da aka yi a birnin Geneva na kasar Switzerland, har ma ya gabatar da jawabi mai taken "Hada kai don gina makomar bil Adama".

A yayin jawabin nasa, shugaba Xi ya ba da shawarwari game da yadda za a gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa, da cimma moriyar juna, inda shawarwarin suka samu amincewa da yaba daga gamayyar kasa da kasa. Masanan kasa da kasa suna ganin cewa, shawarwarin da shugaba Xi ya bayar sun nuna hanyoyin da za a bi don neman ci gaba.

Masanin harkokin yankin arewa maso gabashin Asiya da kuma manufofin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai na kwalejin kimiyyar kasar Rasha Vladimir Matveev ya ce, kiran da aka yi na gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa domin samun ci gaban kasa da kasa cikin hadin gwiwa, ya samu amincewar galibin kasashen duniya

Shehun malamin jami'ar Nairobi ta kasar Kenya Garrishon Ikiara ya ce, jawabin da shugaba Xi Jinping ya yi ya nuna cewa, kasar Sin ta mai da hankali sosai kan huldar dake tsakaninta da kasashe masu tasowa, kuma burin kasar Sin na gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa ya nuna matsayinta na babbar kasa mai tasowa a duniya, da kuma fatanta na shimfida zaman lafiya a fadin duniya, da kuma aniyar kasar ta yin hadin gwiwa da kasa da kasa domin cimma moriyar juna. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China