in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kaddamar da harin ta'addanci a Afirka ta Kudu, in ji Birtaniya
2016-06-07 10:33:08 cri
Bayan gargadin yiwuwar kaddamar da harin ta'addanci da ofishin jakadancin kasar Amurka dake Afirka ta Kudu ya yi a ranar 4 ga watan nan, a jiya Litinin nan, shi ma ofishin jakadancin kasar Birtaniya dake Afirka ta Kudu ya sake nanata wannan gargadi.

Cikin wani bayanin gargadi da ofishin ya fitar, ya ce akwai matukar yiyuwar 'yan ta'adda za su kaddamar da harin ta'addanci a Afirka ta Kudu, ko da yake ba a iya tabbatar da inda za su kaiwa harin ba, amma mai iyuwa ne ya zamo a wasu wuraren saye da sayarwa, inda baki 'yan kasashen waje kan kai ziyara a birnin Johannesburg ko Cape Town.

Haka kuma, bayanin ya ce a halin yanzu, 'yan kasar Birtaniya na fuskantar karin kalubalen ta'addanci, sakamakon rikice-rikicen dake aukuwa a kasashen Iraqi da Syria, don haka ya kamata a kara mai da hankali kan wannan lamari.

Dangane da wannan batu, ministan tsaron kasar Afirka ta Kudu David Mahlobo, ya bayyana a jiya Litinin cewa, hukumomin tsaron kasarsa za su ci gaba da yaki da masu tsattsauran ra'ayi, da 'yan ta'adda, a wani mataki na tabbatar da tsaron rayukan al'ummar kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China