in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jaridun Afirka ta Kudu: Amurka ce ta yi magudi kan batun tekun kudu na Sin
2016-05-27 11:11:52 cri
A kwanan baya, wasu manyan jaridun kasar Afirka ta Kudu sun gabatar da wasu bayanin da wani shahararren mai sharhi kan harkokin duniya na kasar Shannon Ebrahim ya gabata, inda ya bayyana cewa tun asali kasar Sin tana mallakar tsibiran dake tekun kudu, amma daga bisani Amurka ta yi magudi kan wannan batu a boye. Hakan a cewar sharhin ya zama babban dalilin da ya tsananta yanayin da ake ciki a wannan yanki.

Jaridun Star, da Pretoria News, da Cape Times da sauransu wadanda kamfanin yada labarai na "Freedom" dake kasar Afirka ta Kudu ke mallakarsu, sun gabatar da wannan bayani, inda aka furta cewa, Sin tana da ikon mallakar tsibiran tekun kudu, wanda hakan ke da cikakkun shaidun tarihi.

Har wa yau kasar Sin tana kokarin gudanar da shawarwari da wadannan kasashe na yankin tekun kudu dake yunkurin samun ikon mallakar tsibiran a wannan yanki, tare da fidda ra'ayinta na raya tsibirai tare da su, shi ya sa aka tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tekun kudu na Sin.

Dadin dadawa, bayanin ya ce, Amurka ce ta yi magudi kan wannan batu a boye. A cikin shekarun baya da suka wuce, sabo da gwamnatin Amurka dake karkashin jagorancin Barack Obama tana bin tsarin 'Sake samun daidaito a nahiyar Asiya da tekun Pasifik', shi ya sa yanayin da ake ciki a yankin tekun kudun ke kara tsananta.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China