in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
OIC ta jaddada da yaki da ta'addanci da farko
2016-04-16 12:25:44 cri
An rufe taron koli na kungiyar hadin gwiwar kasashen musulmi wato OIC karo na 13 na kwanaki biyu a birnin Istanbul dake kasar Turkiya a ranar 15 ga wata, inda aka zartas da sanarwa, wadda ta jaddada mai da aikin yaki da ko wane irin ta'addanci a matsayin aikin a gaban kome na kasashe membobin kungiyar.

Sanarwar ta jaddada niyyar yaki da ta'addanci ta hanyar hadin gwiwa, da yin Allah wadai da duk wane irin ta'addanci, kana taron ya bayyana ra'ayin kasashe membobin kungiyar na ci gaba da yin hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci.

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdoğan ya bayyana a gun taron manema labaru bayan kammala taron cewa, ta'addanci ya fi kawo babbar illa ga kasashen mulsumi.

Shugaba Erdoğan ya sanar a ranar 14 ga wata cewa, kasashe membobin kungiyar OIC sun amince da shawarar da Turkiya ta bayar game da kafa cibiyar hadin gwiwa ta 'yan sanda ta kungiyar OIC a birnin Istanbul, wadda za ta kasance tsarin hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci da sauran manyan laifuffuka.

Game da halin da ake ciki a kasar Syria, sanarwar ta jaddada nuna goyon baya ga warware batun ta hanyar siyasa bisa tushen sanarwar Geneva, kana ta nuna goyon baya ga MDD da ta jagoranci wannan yunkuri.

Za a gudanar da taron kungiyar OIC na gaba a birnin Banjul na kasar Gambia, ko da yake ba a tsaida lokacin gudanar da shi ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China