in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga kasashen duniya da su bunkasa hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci a yankin Sahel
2016-05-27 16:15:13 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wu Haitao, ya yi kira ga kasa da kasa da su sa kaimi gudanar da hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci a yankin Sahel dake nahiyar Afirka a dukkanin fannoni, tare da goyon baya ga kasashen dake yankin don cimma nasarar wannan manufa.

Kwamitin sulhun MDD ya gudanar da taro game da batun yankin Sahel, inda cikin jawabin da ya gabatar, Wu Haitao ya ce kamata ya yi kasashen duniya su dora muhimmanci kan babbar illar da ayyukan ta'addanci suke haifarwa a yankin Sahel, da kara zuba jari ga yankin don yaki da ta'addanci.

Wu Haitao ya kara da cewa, Sin da Afirka suna da buri iri daya, da moriya ta bai daya. Kana kasar Sin tana fatan ci gaba da kokari tare da kasashen Afirka, don gudanar da ayyukan da za su amfani nahiyar Afirka, ciki har da kasashen yankin na Sahel. Ta hakan ne kuma za a cimma burin samun zaman lafiya da wadata, da kuma bunkasuwa a nahiyar Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China