in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Turkiya ta kai hari kan kungiyar IS a arewacin Iraqi
2016-03-27 13:01:25 cri
Hedkwatar manyan hafsoshin sojan kasar ta Turkiya ta fidda wata sanarwa a ran 26 ga wata cewa, sojojin kasar sun kai hari kan kungiyar IS dake arewacin kasar Iraqi.

Cikin sanarwar, an bayyana cewa, a wannan rana, jiragen saman sojan kasar sun kai hare-hare kan wurare guda hudu na kungiyar IS dake arewacin kasar Iraqi, inda, sojojin suka lalata sansanonin kungiyar guda hudu a yankin, sai dai ba a bayyana adadin rasuwa da jikkatar mutane sakamakon hare-haren ba.

Bugu da kari, an ce, a ran 26 ga wata, dakarun kungiyar IS sun kai farmaki a wani sansanin horaswa na sojojin kasar Turkiya a birnin Mosul dake arewacin kasar Iraqi, lamarin da ya haddasa rasuwar sojan kasar Turkiya guda daya, da jikkata guda. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China