in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen yammaci guda 7 sun sha alwashin karfafa yakin su da IS
2016-01-21 11:07:40 cri
Manyan jami'ai daga kasashe 7 da Amurka ke jagoranta na yaki da kungiyar Daesh wato IS sun yi alkawari a ranar laraban nan na cigaba ga kara karfin harin sojin su na hadin gwiwwa da karfafa farmakin su wajen tumbuke kungiyar.

A taron da suka yi a birnin Paris, ministocin tsaron kasashen Faransa, Amurka, Australia, Jamus, Ingila, Italiya da Netherlands sun tabbatar da kudurin su na karfafa farmakin su a kan kungiyar ta IS domin samar da gaggarumin nasara mai dorewa a kan kungiyar.

A cikin sanarwar bayan taro, mahalarta taron sun yi nuni da bukatar dake akwai na cigaba da kara karfi wajen yakin su da kungiyar IS tare da shirya matakin gaba da za'a yi amfani da shi domin dakushi karfin kungiyar.

Manyan hafsoshin sojin kasashen guda 7 sun kuma amince da yin nazarin ayyukan da suke yi a kai a kai da duba cigaban da aka samu.

A taron manema labarai da suka yi gaba dayan su tare da babban hafsan tsaron kasar Amurka Ashton Carter, da ministan tsaron Faransa Jean Yves Le Drain sun ce kungiyar IS suna ja da baya saboda an samu nasarar lallata kayyayakin su, don haka yanzu lokaci yayi na kara azama gaba daya ta hanyar aiwatar da wani sabon dabara ta soji.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China