in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Turkiya ya soki goyon bayan da Rasha tayi ma shugaban kasar Syriya
2015-12-30 10:03:38 cri
Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan a ranar tarlatan nan ya soki Rasha bisa ga goyon bayan Shugaban kasar Syria Bashar al-Assad da ta yi, ganin da ma dangataka tsakanin Moscow da Ankara ya yi tsami tun lokacin da kasar Turkiya ta harbo wani jirgin saman yaki na kasar Rasha a watan jiya.

Shugaba Erdogon jim kadan kafin ya tashi daga birnin Istanbul zuwa kasar Saudiya don ziyarar aiki ya furta cewa ba yadda za'a yi a ce an goyi bayan gwamnatin kasar da ta hallaka jama'ar ta da ba su ci ba ba su sha ba har sama da 400,000 da makamai na zamani da ma masu guba.

Har ila yau ya zargi wassu kasashen da kara rura wutan rikici ta goyon bayan jam'iyyar demokradia na tarayyar Kurdawa wato PYD na kasar Syriya da kuma bangaren masu dauke da makamai na jam'iyyar YPG.

Kasar Turkiya tana daukan dukkan wadannan jam'iyyu biyu a matsayin na 'yan ta'adda saboda alakar su da tsohuwar jam'iyyar ma'aikata ta Kurdawa wato PKK na kasar ta, abin da ya sa take nuna fargaban zasu iya kafa jihar kurdawa mai cin gashin kanta a arewacin Syria.

Shugaba Erdogab yace kau da ido a kan kisan kare dangi na kungiyoyin 'yan ta'adda kamar su PYD da YPG, don kawai sun ce suna fafutuka ne a kan dakile Daesh wato sunan kungiyar IS da larabci, ya zama rura wutan rikici.

Amurka da Rasha gaba dayan su suna goyon bayan kungiyoyin biyu, saboda ana daukan su a matsayin wadanda suka cancanta wajen yakar kungiyar IS.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China