in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IS ta dauki alhakin kaddamar da hari a fadar shugaban kasar Yemen
2016-01-29 10:32:54 cri
Reshen kungiyar masu kaifin kishin Islama ta IS dake Yemen, ta sanar cewar ita ce ta kai harin kunar bakin wake a fadar shugaban kasar dake kudancin birnin Aden a ranar Alhamis, harin wanda ya hallaka sojoji tara da jikkata wasu da dama.

Reshen IS dake Yemen, ya sanar da hakan ne a wata sanarwa a shafukanta na sada zumunta, inda ta nuna cewar mai kai harin ya fito ne daga kasar Netherland domin kaddamar da harin bam a birnin Aden.

Kusan sojoji 10 dake gadin shugaban kasar harin ya hallaka, ciki harda manyan jami'an fadar shugaban kasar, sannan wasu karin jami'an 20 suka jikkata a lokacin kaddamar da harin, a cewar sanarwar.

Da ma dai kungiyar IS ta sha barazanar kaddamar da hare hare kan shugaban kasar Yemen wanda kasashen duniya suka amince da shi Abdu-Rabbu Mansour Hadi da kuma gwamnatinsa

Masana a kasar ta Yeme sun bayyana cewar, wannan shine karon farko da reshen kungiyar IS dake Yemen ya dauko hayar mahara daga kasashen yammacin duniya don kaddamar da hare hare a Yemen.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China