in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AL ta bukaci Turkiya da ta gaggauta janye sojojinta daga Iraki
2015-12-25 09:51:25 cri
Kungiyar kasashen Larabawa(AL) ta bukaci kasar Turkiya da ta gaggauta janye sojojinta daga yankunan kasar Iraki.

Kungiyar ta yi wannan kiran ne a taron ministocin harkokin waje da ta kira jiya Alhamis a birnin Alkhahiran Masar.

Babban sakataren kungiyar Nabil al-Araby ya ce abin da kasar Turkiyan ta aikata tamkar keta dokokin kasa da kasa ne.

Ko da ya ke kasar Turkiyan ta sanar da cewa, ta fara janye dakarunta daga yankuan kasar ta Iraki sakamakon kiran da shugaban Amurka Barack Obama ya yi wa kasar Turkiya da ta janye dakarun nata. Amma ministan harkokin wajen kasar Iraki ya nace cewa, abin da suke bukata shi ne Turkiya ta gaggauta janyewa a aikace ba wai maganar fatar baki ba.

A farkon watan Disamba ne kasar Turkiya ta jigbe dakarunta a wani sansanin da ke kasar ta Iraki da sunan shirin samar da horo a yakin da ta ke yi da kungiyar IS.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China