in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta nemi taimakon WHO domin shawo kan yaduwar cutar sankarau a kasar
2016-01-29 15:41:55 cri
Ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Ghana ta bayyana cewa, mahukuntan kasar sun roki hukumar lafiya ta duniya ta WHO da ta taimaka musu wajen ganin shawo kan yaduwar cutar sankarau da ta bullo a kasar a kwanakin baya.

Haka kuma, a cewar wani jami'in sashen binciken cututtuka na ma'aikatar lafiyar kasar, an fara ganin alamar barkewar cutar sankarau a birnin Brong Ahafo daga karshen watan Disamba da ya gabata, ya zuwa yanzu, mutane sama da 160 ne a larduna biyar suka kamu da cutar, yayin da mutane 38 suka rasu sakamakon kamuwa da cutar .

Bugu da kari, ma'aikatar kiwon lafiyar kasar ta ce, hukumomin da abin ya shafa sun dukufa yadda ya kamata domin kawo karshen yaduwar cutar a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China