in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar WHO ta gabatar da shirin tinkarar cutar Ebola na shekarar 2015
2015-04-29 15:37:56 cri
Hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO ta gabatar da shirin tinkarar cutar Ebola na shekarar 2015 a birnin Geneva a ranar Talata nan, inda ta ce, za a hana yaduwar cutar Ebola a kasashe masu fama da ita a karshen wannan shekarar.

Hukumar WHO ta bayyana cewa, matakan da aka dauka sun cimma nasarar hana karuwar yawan mutanen da suka kamu da cutar, don haka burin shirin tinkarar cutar na shekarar 2015 ya hada da hana yaduwar ta a kasashe masu fama da ita, har ma a sauran kasashe da yankuna a duniya, da kuma inganta hidimar badaaikin jinya don kara karfin tinkarar cutar da dai sauransu.

Bisa kididdigar alkaluman da hukumar WHO ta gabatar a wannan rana, an ce, yawan mutanen da aka zargi yi shakkar cewa su kamu da cutar Ebola ko kuma tabbatar da sun kamukamuwarsu da cutar ta Ebola a kasashen Guinea, Liberia da Saliyo ya kai 26,277, yayin da mutane wasu 10,884 a cikinsu suka mutu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China