in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO: Kamata ya yi kasashen Afirka su kara zuba jari a fannin kula da lafiyar al'umma
2015-05-09 17:30:12 cri
Darakta mai kula da nahiyar Afirka ta hukumar lafiya ta duniya Matshidiso Moet, ta ce ya zama wajibi kasashen dake nahiyar su kara zuba jari a fannin kiwon lafiyar al'umma, domin kare jama'a daga nau'o'in cututtuka, da annoba dake sabbaba rasuwar dubban mutane a nahiyar.

Matshidiso ta ce shirin hukumar WHO na shekarar bana, wanda ke maida hankali ga kare lafiyar mata, yara kanana, da sauran al'umma, zai yi matukar tasiri wajen dakile mace-mace dake da nasaba da cututtukan da ake iya kaucewa.

A cewar ta wannan manufa ta kunshi mai da kiwon lafiya a matsayin ginshikin inganta burin kare rayukan al'umma nan da shekarar 2030. A daya hannun tsarin na da burin ganin an kara yawan kudaden da ake warewa harkokin kiwon lafiya ga kowa da kowa.

Matshidiso ta ce tuni kasashe kamar Ghana da Rwanda, suka fara daukar matakan rage gibin dake tsakanin al'ummun kasashen su a fannin na kiwon lafiya, ta hanyar kafa tsare-tsaren inshorar lafiya. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China