in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta kafa rundunar tsaro ta musamman don gudanar zabe cikin lumana
2016-01-21 10:52:01 cri
Ministan harkokin cikin gidan Ghana Mark Owen Woyongo, a ranar Larabar nan, ya kaddamar da wata tawagar jami'an tsaro ta musamman da za su sa ido don tabbatar da an gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokokin kasar cikin kwanciyar hankali a wannan shekara.

Wannan runduna, ita ce za ta jagoranci duk wasu ayyuka na liken asiri dangane da zaben, da kuma samar da duk wasu muhimman bayanai ga sauran jami'an tsaron kasar game da sha'anin zaben.

Woyongo, ya bukaci dukkannin hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki a kasar, da su tsara dukkannin dabarun da za su taimaka waje samun nasarar zabukan kasar cikin lumana, kamar yadda suka saba aiwatarwa a shekarun baya.

Tawagar dai ta kunshi wakilai daga dukkanin bangarori da hukumomin tsaro na shiyyoyi da majalisar koli ta kasar.

Mai rikon mukamin babban sifeton 'yan sandan kasar John Kudalor, ya ce, batun zabe al'amari ne mai muhimmanci, wanda ya fi karfi a danganta shi da duk wani soki burutsu ko da ta husuma, wanda ka iya haifar da barazanar tsaro ga kasar, ya kara da cewar za su dauki dukkanin matakan da suka dace kan duk wasu kungiyoyi ko jamiyyun siyasa masu daukar doka a hannun su. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China